✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Bethel Baptist: Dalibai 2 sun tsere daga hannun ’yan bindiga

’yan bindigar na neman fansa ta N500,000 kan kowane dalibi daya.

Biyu daga cikin daliban Sakandiren Bethel Baptist sun shaki iskar ’yanci bayan sun tsere daga hannun ’yan bindigar da suka sace su makonni biyu da suka gabata.

Wani babban ma’aikaci a makarantar da ya bukaci a sakaya sunansa, shi ne ya tabbatar da hakan yayin zantawa da Aminiya a ranar Alhamis.

Bayanai sun ce daliban biyu da suka tsere wadanda ’yan uwan juna ne a halin yanzu suna samun kulawa a wani asibiti da ba a fayyace sunansa ba.

“Tabbas dalibai biyu sun kubuta daga hannun wadanda suka yi garkuwa da su,” a cewar majiyar.

Jami’in Hulda da Al’umma na Rundunar ’Yan sandan Jihar Kaduna, ASP Jalige Muhammad, ya tabbatar da faruwar lamarin.

A cewar ASP Jalige, jami’an ’yan sanda sun tsinto daliban ne a cikin jeji kuma aka yi gaggawar mika su asibiti.

“Sun tsere daga hannun ’yan bindigar sannan jami’anmu suka tsinto su a cikin daji, inda suka mika su zuwa asibiti, a cewar ASP Jalige.

Ana iya tuna cewa, a ranar 5 ga watan Yuli ne ’yan bindiga sun kai hari makarantar sakandiren Bethel Baptist High School da ke Jihar Kaduna.

’Yan bindigar da suka kai hari sun sace dalibai fiye da dari a sakandiren da ke hanyar Kaduna zuwa Kachia a Karamar Hukumar Chikun da ke Kudancin Kaduna.

Rahotanni sun ce ’yan bindigar suna neman fansa ta naira dubu dari biyar kan kowane dalibi daya da ke tsare a hannunsu.