✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Biden ya kammala ziyarar Gabas ta Tsakiya

Ita ce irinta ta farko tun bayan dare wa madafun iko watanni 18 da suka gabata.

Shugaban Amurka Joe Biden, ya kammala ziyarar aiki da ya soma tun makon jiya a yankin Gabas ta Tsakiya.

Wannan ziyara ta kwanaki hudu da Biden ya kai Gabas a Tsakiya, ita ce irinta ta farko tun bayan dare wa madafun iko watanni 18 da suka gabata.

Biden ya karkare ziyarar ce da halartar taron koli na Majalisar Kawancen Hadin Kai na kasashen yankin Gulf mai mambobin shida.

A taron wanda kuma kasashen Masar da Jordan da Iran da suka halarta, Biden ya jaddada matsayar Amurka na ci gaba da zama babbar kawa ga kasashen yankin.

Mahukunta a Isra’ila na fatan wannan ganawa da shugaba Biden ya yi da shugabannin kasashen ya taimaka wajen samar da kungiyar kawancen tsaro da ita ma za a saka ta a ciki, a wani mataki na kara hadin kai domin tunkarar barazanar da kasar Iran ke da shi ga yankin.

A ganawar da ya yi da Yarima mai jiran gado na Saudiyya, Mohammed bin Salman, Joe Biden ya tabo batun mutunta ’yancin dan adam, da batun tsagaita wuta a kasar Yemen gami da batun kisan dan jaridar nan, Jamal Khashoggi.