✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Bikin Sallah: NSCDC ta jibge jami’ai 614 a Gombe

An jibge dakarun don sanya ido a lokutan bukukuwan sallah da za a gudanar.

A bukukuwan Sallah da ake shirin farawa a ranar Litinin a Jihar Gombe, Hukumar Tsaron Farin Kaya ta Civil Defence (NSCDC) ta jibge dakarunta 614 a wurare daban-daban a Jihar.

Kwamandan hukumar a Jihar, Waziri Babagoni Goni ne, ya bayyana hakan ga manema labarai, inda ya ce tuni hukumar ta tura jami’ai 614 don sanya ido da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a lokacin shagulgulan Sallah.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Kwamandan hukumar ya aike wa manema labarai ta hannun Kakakin hukumar, DSC Buhari Sa’ad.

A cewarsa tura jami’an yana nuni ne da cewa za su yi aiki a wuraren don samar da tsaro bisa umarnin da babban Kwamandan hukumar na kasa Abubakar Ahmed Audi, ya umarce su.

Ya kuma ce an tura jami’an ne a masallatai, wuraren shakatawa, tashohin mota, kasuwanni da sauran wuraren taron jama’a.

Waziri, ya taya daukacin al’ummar musulman duniya murnar zagayowar karamar sallah da fatan za a yi bikin sallah lafiya.

Sannan ya hori jami’an hukumar da su kasance masu yin aiki bisa tsarin doka su kuma kare hakkin dan adam.