✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Hotunan Bikin Ranar Tunawa da ’Yan Mazan Jiya na 2021

Yadda aka yi bikin Ranar Tunawa da 'Yan Mazan Jiya na 2021

A ranar Juma’a ce aka yi bikin Ranar Tunawa da ’Yan Mazan Jiya ta Najeriya.

Ranar 15 ga watan Janairun kowace shekara ce aka ware domin tunawa da ’yan Najeriya da suka sadaukar da rayuwarsu domin kare martabar Najeriya da al’ummarta.

An zabi ranar ce kasancewarta makamanciyar ranar da aka yi aka yi wa Firimiyan Arewa na farko, Alhaji Sir Ahmadu Bello Sardauna, Sakkwato da kuma Fira Minista na Farko, Sir Abubukar Tafawa Balewa kisan gilla.

Ga kadan daga hotun bikin na shekarar 2020 da Aminiya ta samo:

Manyan Hafsoshin Tsaro sun kawo gaisuwa ga Shugaba Buhari a lokacin taron.
Sojoji na raka Buhari a lokacin faretin Ranar Tunawa da ‘Yan Mazan Jiyata 2021
Wata soja daga cikin ‘yan badujala da suka tarbi Shugaban Kasa a wurin taron.
Buhari da manyan jami’an gwamnati da suka halarci taron karrama ‘yan mazan jiya sun kame a lokacin da ake yin taken Najeriya.
Shugaban Kasa na duba sojoji a yayin faretin Ranar Tunawa da ‘Yan Mazan Jiya na 2021
Shugaba Buhari ya ajiye fure, alamar girmamawa ga ‘yan mazan jiya da rasa rayukansu saboda Najeriya.
Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan (da fararen kaya) da Shugaban Majalisar Wakilai, Femi Gbajabiamila suna ajiye furen kararma ‘yan mazan jiya.
Manyan jami’an Gwamnatin Tarayya a bayan Shugaba Buhari yana sanya hannu a kan rajistar mahalarta.