✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

‘Binciken Magu ya nuna ba wanda ya fi karfin doka’

Fadar Shugaban Kasa ta ce binciken da wani kwamitinta ke yi wa mukaddashin shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta EFCC, Ibrahim Magu,…

Fadar Shugaban Kasa ta ce binciken da wani kwamitinta ke yi wa mukaddashin shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta EFCC, Ibrahim Magu, a kan kudaden da aka kwato na nuna babu wanda ya fi karfin bincike a gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari.

Wata majiya a fadar ta ce binciken na nuna yadda gwamnatin ke mayar da hankali wajen tabbatar da yin komai a fili kuma zai ba Magu dama ya wanke kansa daga zarge-zargen da ake masa.

Majiyar ta kara da cewa, “Kwamitin da ke binciken zarge-zargen kan mukaddashin shugaban hukumar ya zauna na tsawon wasu makonni.

“Saboda a tabbatar da adalci a binciken, akwai bukatar a ba Magun damar kare kansa daga wadannan manya-manyan zarge-zargen.

“A gwamnatin Muhammadu Buhari, babu, na kara fada babu wanda ya fi karfin bincike.

“Binciken na kokari ne ya tabbatar da yin komai a fili ba tare da boye-boye ba. Ga wanda yake rike da muhimmin mukami kamar na shugaban EFCC, ya kamata a ce ba shi da kashi a gindi”, inji majiyar.

To sai dai zuwa lokacin rubuta wannan rahoto masu magana da yawun shugaban kasa sun ki cewa uffan a kan batun, musamman kan zargin korar Magu.

A wani labarin kuma, kwamitin da ke binciken Magun kan zargin badakalar karkashi shugabancin Mai Shari’a Ayo Salami ya ci gaba da zamansa a ranar Talata a dakin taro na fadar shugaban kasa.

Sai dai kamar ranar litinin, an hana manema labarai shiga wurin.

Magu dai na fuskantar zarge-zargen da ministan shari’a kuma babban lauyan gwamnati, Abubakar Malami ke masa da ke da nasaba da cin hanci da rashawa.

A ranar Litinin dai fadar shugaban kasa ta ce ba kama Magun aka yi ba, gayyatar sa aka yi don ya amsa tambayoyi.