✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Biyafara: Gwamnonin Kudu maso Gabas sun nesanta kansu da ’yan IPOB

Gwamnonin sun kuma ce suna goyon bayan Najeriya a matsayin kasa daya.

Gwamnonin Jihohin yankin Kudu maso Gabashin Najeriya sun nesanta kansu daga masu fafutukar ballewa daga Najeriya domin kafa kasar Biyafara.

Sun kuma yi Allah-wadai da hare-haren da suka biyo bayan fafutukar, wadanda suka janyo asarar rayuka da dukiyoyi masu dimbin yawa.

Idan dai za a iya tunawa, haramtacciyar kungiyar nan ta ’yan awaren Biyafara ta IPOB ta jima tana kokarin ganin yankin ya balle daga Najeriya.

To sai dai Gwamnonin sun yi wani taro a Enugu ranar Asabar domin tattauna matsalolin da suka addabi yankin da kuma hanyoyin lalubo bakin zaren.

Shugaban Gwamnonin, kuma Gwamnan Jihar Ebonyi, David Umahi wanda ya yi magana a madadin takwarorin nasa ya ce, “Muna Allah-wadai kan dukkan abubuwan da masu fafutukar nan suke yi na tada-zaune-tsaye, ko a Kudu maso Gabas ko ma a kowanne yanki.

“Muna jaddada cewa mana tare da su, ba da yawunmu suke yi ba.

“Zargin da ake yi cewa jagororin wannan yankin sun yi gum da bakinsu a kan lamarin ba gaskiya ba ne.

“Mu ’yan kabilar Ibo, muna jaddada mubayi’armu ga Najeriya a matsayin kasa daya dunkulalliya, wacce za a tabbatar da adalci, ’yanci, soyayya da kaunar juna a cikinta,” inji Gwamnonin.