✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Boko Haram ta hallaka mutum 13 a arewacin Kamaru

Akalla mutane 13 ne wani harin kunar bakin wake na kungiyar Boko Haram ya hallaka bayan fashewar wani bom a wani kauye dake Arewacin Kamaru.

Akalla mutane 13 ne wani harin kunar bakin wake na kungiyar Boko Haram ya hallaka bayan fashewar wani bom a wani kauye dake Arewacin Kamaru.

Rahotanni sun ce dukkan wadanda harin ya ritsa da su fararen hula ne, yayin da takwas daga cikinsu kuma yara ne kanana.

Kamfani Dillancin Labarai na AFP ya ruwaito cewa wata mace ce ’yar kunar bakin wake ta tayar da bom din dake jikinta a wani kauye a Arewacin kasar.

Muna tafe da karin bayani…