✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Buhari na jagorantar taro kan sha’anin tsaro a Fadar Shugaban Kasa

Taron dai na zuwa ne a daidai lokacin da Najeriya ke fuskantar kalubalen tsaro a kusan kowanne bangare na kasar.

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na jagorantar wani muhimmin taro kan harkokin tsaro tare da Mataimakinsa, Farfesa Yemi Osinbajo a Fadar Aso Rock dake Abuja.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya ya rawaito cewa taron dai na gudana ne a Dakin Taron Uwar-Gidan Shugaban Kasa sakamakon kwaskwarimar da ake yi a babban dakin taro na fadar shgaban.

Taron dai yana kuma samun halartar Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha da Shugaban Ma’aikatan Fadar Shaugaban Kasa, Farfesa Ibrahim Gambari, Ministan Tsaro, Bashir Magashi da kuma Mai ba Shugaban Shawara Kan Harkokin Tsaro, Manjo Janar Babagana Monguno mai ritaya.

Sauran masu halartar taron sun hada da Babban Hafsan Tsaro, Janar Lucky Irabor, takwaransa na Kasa, Lafatanara Janar Ibrahim Attahiru, da na Ruwa, Bayis Admiral Auwal Zubairu da na Sama, Eya Mashal Ishiaka Oladayo Amao da kuma mai rikon mukamin Babban Sufeton ‘Yan Sandan Najeriya, Usman Alkali Baba.

Babu dai cikakken bayani kan abubuwan da taron zai fi mayar da hankali, amma ana gani ba zai rasa nasaba da irin matsalolin tsaron dake kara tabarbarewa a kullum ba.

Taron dai na zuwa ne a daidai lokacin da Najeriya ke fuskantar kalubalen tsaro a kusan kowanne bangare na kasar.