Shugaba Muhammadu Buhayi ya sanar da cewa gwamnatinsa ta kaddamar da wasu manyan ayyuka uku da za ta aiwatar.
A wani sako da Shugaban kasar ya wallafa a shafinsa na Twitter, ya ce ayyuka da ya kaddamar za su hada da aikin shimfida sabon layin dogo daga Fatakwal zuwa Maiduguri.
- ’Yan bindiga sun sake kai hari Neja, mutum 18 sun fada tarko
- Ganduje ya roki Gwamnatin Tarayya ta sake bude filin jirgin saman Kano
Sauran ayyukan da Shugaban ya kaddamar sun hada da tashar jirgin ruwa ta Bonny a Jihar Ribas da kuma babbar tashar jirgin kasa a birnin Fatakwal da za a rika jigilar kayayyakin da aka samar a cikin gida.
Kazalika, ya ce layin dogon da za a shimfida daga Fatakwal zuwa Maiduguri zai zama hanyar jigilar kayayyakin da aka samar sannan kuma za ta bunkasa sufurin cikin gida gami da shigowa da fitar da kaya zuwa ketare.