✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Buhari ya gana da Jonathan kan rikicin Mali

Buhari ya bukaci a kai zuciya nesa domin magance rikicin siyasar Mali.

Shugaba Buhari ya karbi bakuncin tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan wanda shi ne wakili na musamman kuma mai shiga tsakani na ECOWAS a kasar Mali.

Buhari, a yayin ganawar da aka gudanar a Abuja, kan rikicin siyasa a kasar, ya yi kira ga bangarorin da su hada kai don samun zaman lafiya da hadin kan kasar.

A cewarsa, “Yanayin da ake cikin wanda mafi yawan sassan kasar ke hannun masu tayar da kayar baya na bukatar a yi yarjejeniya tare da maido da zaman lafiya, ba kara rura wutar rikicin ba.

“Ina kira ga duk masu ruwa da tsakin su hada kai domin samun zaman lafiya da tsaro a Mali.”

Wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Femi Adesina ya fitar ta ce Jonathan ya yi wa shugaban bayanin halin da ake ciki a Mali bayan ganawa da manyan ’yan siyasa a gabanin taron shugabannin ECOWAS a karkashin Shugabancin Shugaba Nana Akufo-Addo na kasar Ghana.

Ya kara da cewa taron shugabannin kasashen yankin ya zama wajibi don hanzarta samar da ingantacciyar hanyar warware matsalar da ke addabar kasar ta Yammacin Afirka.