✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Buhari ya kawo wa Tinubu rumfar zabensa

Buhari ya kawo wa 'yan takarar APC rumfarsa da ke mahaifarsa a Daura, Jihar Katsina.

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya kawo wa jam’iyyarsa ta APC rumfar zabensa a zaben shugaban kasa da kuma ’yan Majalisar Dokoki ta Kasa.

A rumfar zaben Buhari ta Sarkin Yara A, dan takarar shugaban kasa na APC ya samu yi nasara da tazara mai yawa, inda ta samu kuri’a 184 a yayin da babba jam’iyyar adawa ta PDP ta samu 51 sai NNPP kuri’a 37.

A zaben sanata da aka gudanar rumfar zaben Buhari da ke ke mahaifarsa a Daura, Jihar Katsina, jam’iyyar APC ta Shugaba APC na da 215, dai PDP 51 sa nnan NNPP 4.

Dan takarar Majalisar Wakilai kuma, APC ta samu gagaruamr nasara da kuri’a 236, sai PDP ta samu 25, NNPP kuma kuri’a hudu.