✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Buhari ya nada Buba Marwa a matsayin sabon Shugaban NDLEA

Garba Shehu ya ce nadin n Buba Marwa ya fara aiki ne nan take.

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya amince da nadin tsohon Gwamnan Jihar Legas na mulkin soja, Birgediya Buba Marwa (mai ritaya) a matsayin sabon Shugaban Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA).

Kakakin Shugaban Kasar, Malam Garba Shehu ne ya tabbatar da hakan a ranar Asabar yayin da yake amsa tambaya kan gaskiyar jita-jitar da ake yadawa kan nadin.

Garba Shehu ya ce,“Gaskiya ne Shugaban Kasa ya amince da nadin Buba Marwa a matsayin sabon Shugaban Hukumar NDLEA.”

Ya ce nadin nasa ya fara aiki ne nan take.

Kafin nadin nasa, Buba Marwa shi ne shugaban Kwamitin Dake ba Shugaban Kasa Shawara kan Yaki da Miyagun Kwayoyi (PACEDA) tsakanin shekarun 2018 zuwa 2020.

A lokacin dai ya ba da gudunmawa matuka wajen tsara jadawalin yadda za a kawo karshen ta’ammali da miyagun kwayoyi a Najeriya.

Ya yi karatunsa ne a Makarantar Sojoji (NDA) da ke Kaduna, kafin daga bisani ya wuce zuwa Jami’o’in Harvard da ke Birtaniya da ta Pittsburgh a Amurka inda ya yi digirorinsa na biyu a sassa daban-daban.