✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Buhari ya nada kwamitin da zai sasanta da Twitter

Ministocin Najeriya shida za su tattauna a teburin sulhu da Twitter.

Shugaba Muhammadu Buhari ya nada kwamitin da zai zauna a teburin sulhu da Twitter domin tattauna sabanin da ya kai ga an dakatar da amfani da shafin a Najeriya.

Wata sanarwa da mai taimaka wa shugaban kasar kan harkokin watsa labarai, Segun Adeyemi ya fitar a ranar Talata ta ce, an nada kwamitin ne bayan da kamfanin Twitter ya aike da wani rubutaccen sako na neman sasanci da gwamnatin kasar.

Sanarwar ta ce kwamitin ya kunshi Ministan Sadarwa; Isa Pantami, Ministan Shari’a; Abubakar Malami, Ministan Harkokin Waje; Geoffery Onyeama.

Sauran yan kwamitin sun hada Ministan Ayyuka da Gidaje; Babatunde Fashola, Ministan Kwadago da Samar da Ayyuka; Dokta Chris Ngige da wasu wakilai daga hukumomin gwamnati.

Makonni biyu da suka gabata ne Ministan Labarai da Al’adu, Alhaji Lai Mohammed wanda zai jagoranci kwamitin sasancin, ya ce an dakatar da Twitter ne saboda yadda yake bayar da dama ga wadanda ke barazana ga wanzuwar Najeriya a matsayin kasa dunkulalliya.