Shugaba Muhammadu Buhari ya bayar da umarnin tura karin dakarun soji dubu shida zuwa Jihar Zamfara domin a rubanya ayyukan hukumomin tsaro na yaki da ta’addanci a Jihar.
Gwamna Muhammad Bello Matawalle ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya yi wa manema labarai da Yammacin ranar Talata.
- Wayar salula ta N150,000 ta gurfanar da matashi a gaban Alkali
- Kayan Sata: Mutum hudu sun gurfana a gaban Kotu kan N26.5m
- ’Yan bindiga sun sace mutum 55 a kauyukan Katsina
Gwamna Matawalle ya ce wannan umarni na zuwa bayan wata ziyarar aiki ta kwanaki hudu da ya shafe a birnin Abuja inda ya gana da shugaban kasa da kuma sauran masu ruwa da tsaki kan sha’anin tsaro a kasar.
“Bayan tattaunawa da Shugaba Buhari da kuma manyan hafsoshin tsaro a Abuja, an cimma matsayar tura karin sojoji dubu shida zuwa Jihar Zamfara domin agaza wa kokarin da sauran jami’an tsaro ke yi na magance matsalolin tsaro a jihar.
“Nan ba da dadewa ba dakarun sojin za su iso jihar domin sauke nauyin da rataya a wuyansu sannan kuma muna matukar godiya ga Gwamnatin Tarayya a kan wannan mataki da ta dauka.”
“Saboda haka mu a matakin gwamnatin jiha, mun yanke shawarar daukar wadansu matakai da za su fara aiki nan take da suka hada da tabbatar da sarakunan gargajiya sun kasance a masarautunsu domin sanya idanun lura a kan duk wani shige da fice da yake wakana.”
“Sannan kuma mun hana goyon sama da mutum biyu a kan babur daya tare da haramta tafiyar babura a cikin tawaga ko ayari a dukkanin wani kwararo da sako na jihar,” in ji gwamna Matawalle.
A sanarwar da Gwamna Matawalle ya fitar, ya kara tabbatar da haramcin ayyuka ’Yan sa kai a jihar, inda yake cewa duk wanda aka samu da bindiga da sunan ya fito aikin ’yan banga za a hukunta shi.