✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Buhari ya yi ta’aziyyar rasuwar Sarkin Gaya

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bayyana jimaminsa game da rayuwa Sarkin Gaya, Alhaji Ibrahim Abdulkadir. A sakon Buhari na ta’aziyyar rasuwar Sarkin Gaya, mai magana…

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bayyana jimaminsa game da rayuwa Sarkin Gaya, Alhaji Ibrahim Abdulkadir.

A sakon Buhari na ta’aziyyar rasuwar Sarkin Gaya, mai magana da yawunsa, Garba Shehu, ya fitar, ya bayyana mamacin da cewa “yana daga cikin sarakunan kasar nan da suka kare mutucin sarautun gargajiya.”

Mutumin kirki ne da ya hidimta wa al’ummarsa da sadaukar da kai kuma za a jima ana tunawa da shi da hakan.

Ya kuma jajanta wa Masarautar Gaya al’ummar masarautar da kuma Gwamnatin Jihar Kano game da rasuwar tare da addu’ar Allah Ya gafarta masa Ya kuma rahamshe shi.