✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Buhari zai je Nijar taron tattalin arziki

Za a kaddamar da littafi kan shugabancin Buhari, wanda aka fassara da harshen Faransanci

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari zai bar Najeriya a ranar Alhamis din nan zuwa kasar Jamhuriyyar Nijar domin halartar taron tattalin arziki na Kungiyar Tarayyar Afirka (AU).

Fadar shugaban kasa ta sanar a ranar Laraba cewa a lokacin taron, Buhari zai gabatar da jawabi, sannan ya halarci wani taron kaddamar da fassarar littafin da aka yi a kansa, wanda aka fassara zuwa harshen Faransanci.

Sanarwar da hadimin shugaban kasa Garba Shehu, ya fitar ta ce, “Shugaba Muhammadu Buhari zai kai ziyarar aiki birnin Niamey, hedikwatar kasar Nijar domin halartar Babban Taron Kungiyar Tarayyar Afirka kan Masana’antu da Fadada Tattalin Arziki.

“Zai kuma halarci zaman da za a yi kan Yarjejeniyar Kasuwanci Maras Shinge Tsakanin Kasashen Afirka (AfCFTA).”

Ya kara da cewa shugaban, wanda zai tashi daga Abuja a ranar Alhamis 24 ga Nuwamba, 2022, “Zai kuma kaddamar da wani titi da Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta sanya wa sunansa, ‘Titin Muhammadu Buhari’.

Ya je gabanin taron na AU Buharin zai halarci taron kaddamar da fassarar Faransanci na littafin ‘Muhammadu Buhari: Kalubalen Shugabanci a Najeriya’ (Muhammadu Buhari: The Challenges of Leadership in Nigeria).

Wani malamin Nazarin Harkokin Kasashe a Jami’ar George Mason da ke Arewacin Virginia a kasar Amurka, Farfasa John Paden, ne mawallafin littafin.