✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Buhari zai kaddamar da aikin shimfida layin dogo daga Kano zuwa Maradi

Za a fara aikin mai wa'adin wata 36 a ranar Talata, 9 ga Fabrairu, 2021.

Shugaba Muhammadu Buhari zai kaddamar da aikin shimfida titin jirgin kasa daga Arewacin Najeriya zuwa Maradi a Jamhuriyar Nijar ranar Talata.

Layin dogon da Gwamnatin Tarayya ta ba da aikin sa ga kamfin Mota-Engil na kasar Jamus, a kan Dala biliyan biyu zai tashi ne daga Kano ya keta ta Jihohin Jigawa da Katsina ya dangana da Jihar Maradi a Jamhuriyar Nijar.

‘‘Ina farin cikin sanar da cewa Shugaba Buhari zai kaddamar fara aikin shimfida layin dogo daga Kano zuwa Maradi, a ranar Talata; Aikin ya kankama,’’ inji Ministan Sufuri, Rotimi a ranar Asabar.

A Jihar Katsina ce Buhari zai kaddamar da fara aikin titin jirgin da zai biya ta garuruwan Danbatta a Jihar Kano; Kazaure a Jihar Jigawa; da kuma Daura, Mashi, Katsina da Jibiya a Jihar Katsina kafin ya shiga Jamhuriyar Nijar.

A watan Janirun 2021 ne Majalisar Zartarwa ta Tarayya ta amince da aikin mai tsawon kilomita 283.8 wanda aka sanya wata 36 a matsayin wa’adin kammaluwarsa.

Bayan amincewar, Amaechi ya wakilci Gwamnatin Tarayya wurin sanya hannu a kan yarjejeniyar aikin wanda Manajan Daraktan kamfanin Mota-Engil da zai yi aikin, Antonio Gvoea ya rattaba hannu a madadin kamfanin.

Tun a lokacin wasu ’yan Najeriya sun yi ta ce-ce-ku-ce kan amfani shimfida titin jirgin kasar ga tattalin arzikin Najeriya alhali ba a riga a sada wasu sassan Najeriya ta titin jirgin kasa ba.

Amma a jawabinsa, Amaechi ya ce za a sada layin dogon da tituna ta yadda hakan zai taimaka wajen bunkasa tattalin arziki da abubuwan more rayuwa a kasar.

Amaechi ya kara da cewa kamfanin zai kuma gina wata jami’a a Najeriya a yayin shimfida titin jirin, sai dai bai yi karin bayani game da hakan ba.