✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Buhari zai tafi Landan ganin Likita

Buhari ya sha tafiya Landan domin duba lafiyarsa.

Shugaba Muhammadu Buhari ya shirya sake tafiya birnin Landan domin ganin Likita.

Buhari zai kama hanyarsa ta zuwa birnin Landan a yau Litinin kamar yadda Fadar Gwamnatin Najeriya ta tabbatar.

Kakakin shugaban, Femi Adesina a sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter ya ce ana saran Buhari zai dawo gida a cikin mako na biyu na watan Nuwamba.

Ba wannan ne farau ba domin kuwa Buhari ya sha tafiya Landan domin duba lafiyarsa tun lokacin da ya fara jagorantar kasar.

A 2017, Buhari ya kwashe kwanaki 150 a Birtaniya a wata tafiyar duba lafiyar da ba a bayyana abin da ke damun shi ba.

Buhari ya kara komawa Birtaniya a watan Mayun 2018 domin ganin liktansa, inda ya yi kwana hudu kacal a kasar.

A watan Nuwambar 2020 ne, mai dakin Shugaban Kasar, Aisha Buhari, ta ce akwai bukatar inganta bangaren lafiya a Najeriya domin a rage tafiye-tafiyen neman magani kasashen waje.