✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

City ta kama hanyar lashe Firimiyar Ingila

A halin yanzu dai City ta bai wa Liverpool ratar maki 3 a teburin Firimiya.

Kungiyar Manchester City ta kama hanyar lashe gasar Firimiyar Ingila bayan ta lallasa Newcastle United da ci 5-0 a ranar Lahadin nan.

Wannan nasara da City ta samu ta kara mata karfin gwiwar lashe gasar ta bana la’akari da yadda Liverpool ta barar da damar ta ranar Asabar a karawar da ta yi da Tottenham wanda aka tashi 1-1.

’Yan wasan City zazzaga wa Newcastle United kwallaye 5 sun hada da Aymeric Laporte da Rodri da Phil Foden da kuma Raheem Sterling wanda ya jefa kwallon farko da ta karshe a wasan.

A halin yanzu dai City ta bai wa Liverpool ratar maki 3 a teburin Firimiya.

Yanzu haka Man City na da maki 86 a wasanni 35, yayin da Liverpoll ke da maki 83 a daidai lokacin da ya rage wasanni 3 a kammala gasar baki daya.

Chelsea na ci gaba da zama a matsayi na 3 da maki 67, yayin da Arsenal ke matsayi na 4 da maki 66, sai kuma Tottenham da maki 62 a matsayi na 5, Manchester United na matsayi na 6 da maki 58.