✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Croatia ta doke Maroko a neman mataki na 3 a Gasar Cin Kofin Duniya

Maroko ta yi rashin nasara ne da ci biyu da daya

Tawagar kasar Croatia a ranar Asabar ta doke takwararta ta kasar Maroko da ci biyu da daya a fafatawar neman mataki na uku a Gasar Cin Kofin Duniya da ke gudana a kasar Qatar.

Dan wasan Croatia, Josko Gvardiol, shi ne dai ya fara zura wa kasarsa kwallo a raga bayan minti bakwai da take wasan, wanda aka fafata a filin wasa na Khalifa, amma Achraf Dari ya farke tun ba a je ko ina ba.

Sai dai kwallon da Croatia ta kara jefawa a karo na biyu tun kafin zuwa hutun rabin lokaci ya sanya ta zama kasa ta uku a gasar, wacce karo na 11 ke nan wata kasa daga nahiyar Turai na kammalawa a matakin.

A nata bangaren kuwa, Maroko ita ce kasar Afirka ta farko a tarihi da ta taba zuwa matakin wasan dab da na karshe tun da aka fara gasar.

Yanzu dai ranar Lahadi mai za a fafata wasan karshe a gasar tsakanin kasashen Faransa da Argentina.

Wannan dai shi ne karon farko a tarihi da wata kasar Larabawa da ke yankin Gabas ta Tsakiya da ta shirya gasar tun da aka fara ta a tarihi a sherar 1930.