✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Cutar murar tsintsaye ta sake barkewa a Najeriya

Tuni dai aka farfado da cibiyoyin da za su fara kula da dabbobin da suka kamu a dukkan jihohi

Gwamnatin Tarayya ta yi gargadin cewa cutar nan mai tsanani dake kama dabbobi ta murar tsintsaye ta sake barkewa a Najeriya.

Daraktan Sashen Kula Da Lafiyar Dabbobi da Yaki da Kwari na Ma’aikatar Aikin Gona da Raya Karkara ta Kasa, Olaniran Alabi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis.

Daraktan ya ambato Cibiyar Bincike Kan Lafiya Dabbobi ta Kasa dake Vom a jihar Filato wacce ya ce ita ce ta tabbatar da hakan a wani rahoto da ta karba ranar 29 ga watan Janairun da ya gabata.

Ya ce tuni ma’aikatar ta farfado cibiyoyin da za su fara kula da dabbobin da suka kamu a dukkan jihohi 36 na Najeriya.

“Cutar ta barke ne a wasu gidajen gona guda biyu inda dabbobi da dama ciki har da jiminoni, kaji, talo-talo, dawisu da kuma zabi suka kamu a jihar Kano.

“Bugu da kari, a cikin mako daya, an sake samun rahotannin barkewar cutar a wasu gidajen gona dake Jos a jihar Filato, wanda hakan ke nuna cewa cutar na ci gaba da yaduwa kenan,” inji sanarwar.

Cutar dai a tsakanin shekarun 2005 zuwa 2006 ta yi sanadiyyar asarar dabbobi da dama sakamakon kamuwa da ita, lamarin da ya tilasta kashe su domin takaita yaduwarta.