✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Dalibin likitancin da ke sana’ar abinci saboda yajin aikin ASUU ya rasu

Dalibin nan da ya kama sana’ar sayar da abinci a sakamakon yajin ASUU, Usman Abubakar-Rimi, ya kwanta dama. Kafin rasuwarsa, marigayin dalibi ne a ajin…

Dalibin nan da ya kama sana’ar sayar da abinci a sakamakon yajin ASUU, Usman Abubakar-Rimi, ya kwanta dama.

Kafin rasuwarsa, marigayin dalibi ne a ajin karshe a fannin likitanci a Jami’ar Usmanu Danfodiyo ta Sakkwato (UDUS).

Ya kama sana’ar sayar da abinci ne don maganin zaman kashe wando ganin cewa yajin aikin ASUU ya ki ce, ya ki cinyewa.

Abubakar-Rimi ya bude shagon cin abinci ne a birnin Sakkwato inda yake sarrafa rakiyar yara ga mabukata.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ce, Usman ya rasu ne a ranar Laraba bayan fama da takaitaccen rashin lafiya.

Amma sai a ranar Asabar aka tabbatar wa NAN batun rasuwar, kuma tuni aka yi jana’izar marigayin kamar yadda addinin Musulunci ya tanada a mahaifarsa, Rimi da ke Jihar Katsina.