✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Dodo ya kai hari, ya kashe mutum a masallaci

Mabiyan dodo sun bindige mutum daya, sun jikkata wasu da dama a masallaci.

An bindige mutum daya tare da jikkata wasu da dama a yayin da suke tsaka da ibada a wani masallaci a garin Osogbo, Jihar Osun.

Mutanen na tsaka da gudanar da addu’o’i na musamman a karkashin wata rumfa a masallacin ne wani dodo da mabiyansa suka far musu a ranar Lahadi.

An kai wa masu ibadar hari a masallacin ne a yayin da masu dodon suka biya ta harabar Oluode Aranyin, kusa da masallacin.

Maharan sun lalata tagogi da kofofin masallacin a harin da suka kashe wani mutum mai suna Moshood Salawudeen.

Babban Limamin Masallacin, Alhaji Quoseem Yunus, ya ce babu wani sabani a baya tsakanin masu ibadar da masu dodon.

Limamin ya ce da farko sai da masu dodon suka ratsa yankin ba tare da sun far wa masu ibadar ba.

Ya ce bayan sun ci gaba da ibadar tasu a harabar masallacin ne dodon da mabiyansa suka sake dawowa suka far musu.

Wadanda suka samu raunuka a yanzu haka suna kwance a asibiti  a garin Osogbo, yayin da aka ajiye gawar mamacin a dakin ajiyar gawarwaki.

Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Osun, Yemisi Opalola, kuma ba a same ta ba a lokacin hada wannan rahoton.