✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Dubban mutane sun halarci jana’izar Dokta Ahmad Bamba

Dubun dubatar mutane ne suka halarci jana'izar marigayin, wanda ya rasu ranar Juma'a

Dubun dubatar mutane ne suka halarci jana’izar fitaccen malamin addinin Musulunci kuma masanin Hadisi, Dokta Ahmad Ibrahim-Bamba a birnin Kano.

An dai binne malamin, wanda ya rasu ranar Juma’a a Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano (AKTH), a makabartar Dandolo.

Sheikh Bamba ya shahara da gudanar da Tafsirin Alkur’ani da Hadisai a Masallacin Jami’ar Bayero ta Kano (BUK) da kuma makarantarsa ta darul Hadith da ke unguwar Tudun Yola a cikin birnin Kano.

Marigayin, wanda ya rasu yana da shekara 82 a duniya, yana cikin malaman Musulunci masu fada a ji a ciki da wajen Kano.

Ranar Lahadi ne ya yi karatunsa na karshe, har ma ya sanar da hutu na dan wani lokaci, saboda yanayin jikinsa.

Dokta Bamba tsohon malami ne a Sashin Nazarin Harshen Larabci a Jami’ar Bayero da ke Kano, wanda ya ajiye aikin ya kuma dirfafi harkar da’awa da wa’azi gadan-gadan.

A shekarun baya, ana kiran malamin da sunan “Kala Haddasana”, wani lakani da masu halartar karatunsa musamman wanda ya shahara a kai na littafin Muwadda Malik suka sanya masa.

Bayanai sun ce dan asalin kasar Ghana ne kuma a can aka a haife shi.

A wata tattaunawa da wani dansa ya yi da manema labarai, ya ce mahaifinsa “ya dawo Najeriya ne bayan da ya yi karatun digirinsa a Saudiyya, sai ya koma Najeriya ya fara koyarwa a Jami’ar Bayero ta Kano har ya yi digirin-digirgir.

Bajimin malamin ya bar yara 28 zuwa 30 kamar yadda wasu rahotanni suka bayyana.