✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Dukan dan Jarida: Kotu ta Umarci ’yan sanda su yi bincike

Dan Majalisar Tarayya Alhassan Ado Doguwa ya bayani dan jarida saboda ya yi masa tambaya

Wata Kotun majistare a Jihar Kano, ta umarci ’yan sanda su binciki zargin dukan da dan Majalisar Tarayya Alhassan Ado Doguwa, ya yi wa wakilin jaridar Leadership a Kano

Kotun mai lamba 24 mai zamanta a unguwar Gyadi-gyadi ta umarci Mataimakin babban Sufeton ’Yan Sanda na shiyya ta daya da ke Kano, da ta binciki lamarin.

Umarnin na kunshe ne a cikin wata wasika da kotun ta aika wa shugaban shiyyar wacce magatardar kotun ya sa hannu a ranar 1 ga watan Nuwamba.

Hakan ya biyo bayan koken da dan jarida Abdullahi Yakubu ya shigar ta hannun lauyoyinsa Bashir Umar & co a inda ya ke neman kotun da bi masa hakkinsa na cin zarafi da Doguwa ya yi masa ta hanyar dukan sa a yayin gudanar da aikinsa a gidan dan majalisar.

Dan jaridar wanda shi ne babban jami’in kula ofishin jaridar a Kano, ya yi zargin cewa dan majalisar ya naushe shi a yayin da shi da abokan aikinsa ke bakin aikin hira da dan majalisar a gidansa.

Haka kuwa ta faru me yayin da dan jaridar ya tambayi dan majalisar yadda aka yi ya daki Murtala Sulen Garo a yayin wani taro a gidan mataimakin gwamnan Kano.

Dan majalisa Alhassan Ado aka ce, ya fusata a yayin hirar, ya kuma naushi Abdullahi Yakubu wanda a cewarsa, ta kai ga yanzu ba ya ji sosai da kunnensa guda daya.

Lauyoyin sun bukaci da ta gudanar da binciken ne domin daukar mataki na shari’a kan dan majalisar.