✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

El-Rufai ya ba Kwamishina mako 2 ya ajiye mukaminsa

El-Rufai ya ba Dattijo da sauran masu son tsawaya takara a 2023 mako biyu su yi murabus

Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufa’i, ya ba dukkan masu rike da mukaman siyasa a jihar da ke sha’awar tsayawa takara nan da ranar 31 ga watan Maris, su ajiye mukamansu.

A ranar Talata ce dai Muhammad Sani Dattijo, Kwamishinan Kasafin Kudi da Tsare-tsare, kuma tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Gwamnan ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar gwamnan jihar a zabe mai zuwa.

Aminiya ta gano cewa akwai wasu masu rike da mukaman siyasa da dama da ba su kai ga bayyana aniyarsu ta tsayawa takarar ba tukunna.

Amma a cikin wata wasika da Sakataren Gwamnatin Jihar, Balarabe Abbas Lawal, ya fitar, ta ce sabuwar Dokar Zabe ta 2022 wacce Shugaba Buhari ya rattaba wa hannu a kwanan nan, kuma Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta fitar, ta tanadi cewa dole masu rike da mukaman siyasa su ajiye mukamansu kafin zaben fid da gwani na jam’iyyunsu, muddin suna son tsayawa takara.

“Dokar ta yi tanadi karara cewa dole ne wadannan mutanen su ajiye mukamansu kwana 30 kafin ranar gudanar da zaben fid da gwanin kujerar da suke nema.

“Saboda tabbatar da cika wannan sharadin, dukkan masu rike da mukaman siyasa da sauran ma’aikatan gwamnati a Jihar Kaduna da ke son tsayawa kowace irin takara, to dole ne su mika takardar ajiye aikinsu zuwa ga Sakataren Gwamnati, kafin nan da ranar 31 ga watan Maris, 2022,” inji wasikar.