✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

#EndSARS: Masu zanga zanga sun rufe manyan hanyoyin birnin Abeokuta

An gangi jami'an tsaro jefi-jefi da ke jiran tabbatar da kwantar da koda ta kwana.

Daruruwan matasa da ‘yan makaranta gami da masu hidimar kasa ta NYSC ne suka fito zanga zangar kin jinin ‘yan sandan SARS tun da safiyar Juma’a a Abeokuta.

Masu zanga zangan sun rufe hanyar zuwa ofishin gwamnatin jihar Ogun dake Oke Moson daga sashen babban gidan mai na NNPC da ke birnin Abeokuta, hanyar da ta hade birnin Abeokuta da garin shagamu da jihar Legas, lamarin da ya sanya tarin direbobi da fasinjoji yin curko-curko a kan hanya.

Zangan-zangar na ci gaba da gudana cikin salama inda aka hangi jami’an tsaro jefi jefi da ke jiran tabbatar da kwantar da koda ta kwana.

Wakilin Aminiya, Abbas Dalibi, ya kawo muku hotunan yadda zanga zangar ta rika gudana a Abeokuta.