Kungiyar Kwallon Kafa ta Everton ta raba gari da kocinta, Rafael Benitez bayan shafe watanni takwas yana jan ragamar horar da ’yan wasanta.
A watan Yunin bara ne dai Everton ta dauke shi a matsayin sabon kocinta, bayan ya shafe shekaru yana wannan aiki a Liverpool, wadda ta kasance daya daga cikin kungiyoyin da suke bakar hamayya da juna a Ingila.
- ‘Abin da za mu yi la’akari da shi wajen zaben shugaban kasa a 2023’
- Allah Ya yi wa tsohon shugaban Mali Ibrahim Boubacar Keita rasuwa
Sallamar da Everton ta yi wa Benitez a ranar Lahadi na zuwa ne a sakamakon rashin katabus, inda a bayan nan ta yi rashin nasara a wasanni 9 cikin 13 da ta buga a gasar Firimiyar Ingila ta bana.
Bayanai sun ce shan kashin da kungiyar ta yi a hannun Norwich City da ci 2-1 ranar Asabar ne ya kara rura wutar fatattakar Benitez ba tare da wani jinkiri ba.
Tun a wasan ne magoya bayan kungiyar Everton suka rika wake da kururuwar a sallami Benitez la’akari da yadda ya janyo musu abin kunya na rashin nasara a hannun Norwich City da suke gani karanta bai kai irin wannan tsaikon ba.
A yammacin jiya Asabar din ce kungiyar ta kira taron gaggawa inda ta tattauna a kan makomarsa, wanda aka rika rade-radin an fi bayar da rinjayen sallamarsa a taron.
Kafin yanzu, an dai rika ganin cewa dauko Benitez da mai kungiyar ta Everton, Farhad Moshiri ya yi babban kuskure ne wanda masu sharhi a kan wasannin kwallon kafa suka kira lamarin a matsayin caca da makomar kungiyar.
Benitez ya taba fusata magoya bayan Eveton yayin da ya bayyana kungiyar a matsayin ’yar kankanuwar kungiya a lokacin da yake aikin horaswa a Liverpool, kungiyar da ya jagoranra wajen samun nasara a wasan karshe na Gasar Cin Kofin Zakarun Turai da ta fafata da AC Milan a shekarar 2005.
A watan da ya gabata ne Moshori ya tsaya tsayin-daka wajen goyon bayan Benitez, inda ya bukaci a ba shi lokaci ya sauya al’amura a kungiyar idan ta sayi sabbin ’yan wasa sannan wadanda suke jinya suka warke.
Sai dai duk da haka, ba ta sauya zani ba a yayin da kungiyar ta ci gaba da rashin katabus da har ta kai ga hakurin magoya bayan kungiyar ya kai makura.
A yanzu da Benitez ya tattara komatsansa ya kama gabansa, kungiyar tana mataki na 16, inda ta bayar da tazarar maki shida kacal tsakaninta da rukunin wadanda za a kora zuwa buga gasar ’yan dagaji.