✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Everton ta sallami Rafael Benitez

Everton ta bayar da tazarar maki shida tsakaninta da rukunin wadanda za a kora zuwa gasar ’yan dagaji.

Kungiyar Kwallon Kafa ta Everton ta raba gari da kocinta, Rafael Benitez bayan shafe watanni takwas yana jan ragamar horar da ’yan wasanta.

A watan Yunin bara ne dai Everton ta dauke shi a matsayin sabon kocinta, bayan ya shafe shekaru yana wannan aiki a Liverpool, wadda ta kasance daya daga cikin kungiyoyin da suke bakar hamayya da juna a Ingila.

Sallamar da Everton ta yi wa Benitez a ranar Lahadi na zuwa ne a sakamakon rashin katabus, inda a bayan nan ta yi rashin nasara a wasanni 9 cikin 13 da ta buga a gasar Firimiyar Ingila ta bana.

Bayanai sun ce shan kashin da kungiyar ta yi a hannun Norwich City da ci 2-1 ranar Asabar ne ya kara rura wutar fatattakar Benitez ba tare da wani jinkiri ba.

Tun a wasan ne magoya bayan kungiyar Everton suka rika wake da kururuwar a sallami Benitez la’akari da yadda ya janyo musu abin kunya na rashin nasara a hannun Norwich City da suke gani karanta bai kai irin wannan tsaikon ba.

A yammacin jiya Asabar din ce kungiyar ta kira taron gaggawa inda ta tattauna a kan makomarsa, wanda aka rika rade-radin an fi bayar da rinjayen sallamarsa a taron.

Kafin yanzu, an dai rika ganin cewa dauko Benitez da mai kungiyar ta Everton, Farhad Moshiri ya yi babban kuskure ne wanda masu sharhi a kan wasannin kwallon kafa suka kira lamarin a matsayin caca da makomar kungiyar.

Benitez ya taba fusata magoya bayan Eveton yayin da ya bayyana kungiyar a matsayin ’yar kankanuwar kungiya a lokacin da yake aikin horaswa a Liverpool, kungiyar da ya jagoranra wajen samun nasara a wasan karshe na Gasar Cin Kofin Zakarun Turai da ta fafata da AC Milan a shekarar 2005.

A watan da ya gabata ne Moshori ya tsaya tsayin-daka wajen goyon bayan Benitez, inda ya bukaci a ba shi lokaci ya sauya al’amura a kungiyar idan ta sayi sabbin ’yan wasa sannan wadanda suke jinya suka warke.

Sai dai duk da haka, ba ta sauya zani ba a yayin da kungiyar ta ci gaba da rashin katabus da har ta kai ga hakurin magoya bayan kungiyar ya kai makura.

A yanzu da Benitez ya tattara komatsansa ya kama gabansa, kungiyar tana mataki na 16, inda ta bayar da tazarar maki shida kacal tsakaninta da rukunin wadanda za a kora zuwa buga gasar ’yan dagaji.