Hukumar gudanarwar Jami’ar Jos, ta amince da zaben Farfesa Tanko Ishaya a matsayin sabon Shugaban Jami’ar.
Hukumar gudanarwar ta amince da zaben sabon shugaban ne a babban taron da ta gudanar a ranar Juma’a.
- Yadda dakunan kwanan daliban jami’o’in gwamnati suka lalace
- Borno: Sojoji na ragargazar mayakan ISWAP a Askira/Uba
Kafin wannan sabon mukami da aka zabi Farfesa Tanko Ishaya, shi ne Mataimakin Shugaban Jami’ar ta Jos.
Sabon Shugaban Jami’ar ta Jos, zai kama aiki ne daga ranar 1 ga watan Disamba, 2021.
Shi dai Farfesa Tanko Ishaya a yanzu yana da shekara 57 da haihuwa kuma ya fito ne daga garin Zuru na Jihar Kebbi.