✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Fashewar bam ta tarwatsa masu zabe a Abiya

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a wata rumfar zabe lokacin da ake tsaka da zaben cike gurbi ranar Asabar

Masu kada kuri’a da ma’aikatan zabe sun ranta a na kare bayan da fashewar wani sinadari ta haddasa tarwatsa wata rumfar zabe da ke Karamar Hukumar Aba ta Arewa a jihar Abiya.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a wata rumfar zabe da ke Mazaba ta takwas dake Tsaunin Agbor a garin na Aba, a daidai lokacin da ake tsaka da zaben cike gurbi ranar Asabar

Hukumar Zabe ta Kasa Mai Zaman Kanta (INEC) ce dai take gudanar da zaben cike gurbi a Mazabar dan Majalisar Tarayya ta Aba ta Kudu da Aba ta Arewa a jihar.

Ana gudanar da zaben ne bayan mutuwar dan majalisar dake wakiltar mazabar, Hon. Ossy Prestige ranar shida ga watan Fabrairun 2021.

Kafin zaben dai, manyan ’yan siyasar yankin sun yi ta zafafan muhawarori tare da zargin junansu da yunkurin tayar da zaune tsaye lokacin zaben.

Zaben dai na gudana cikin lumana a rumfar zaben har zuwa lokacin da sinadarin wanda ake kyautata zaton bam ne ya fashe.

Aminiya ta gano cewa ba a sami asarar rai ko daya ba sanadiyyar fashewar, ko da yake wasu daga cikin kayan zabe sun lalace.

Ba a dai kai ga tantance ko an dasa bam din ne domin a razana masu zabe a rumfar zaben ba, kuma tuni jami’an tsaro suka yi wa wajen kawanya daga bisani domin dawo da doka da oda.