✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ficewar Kwankwaso: PDP ta rushe shugabancinta a Jihar Kano

Jam'iyyar ta rushe shugabancinta tare sa kafa kwamitin rikon kwarya

Kwamitin Gudanarwar Jam’yyar PDP na kasa (NWC), ya ba da sanarwar rushe shugabancin jam’iyyar a Jihar Kano da ke goyon bayan tsohon Gwamnan Jihar, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

Matakin na zuwa ne bayan umarnin da wata babbar kotu da ke Abuja ta bayar na hana jam’iyyar daukar matakin rushe shugabancin da ke karkashin jagorancin Shehu Wada Sagagi.

A sanarwar da ta fitar ta hannun sakataren tsare-tsare na jam’iyyar, Umar M. Bature, PDP ta ce sun yi la’akari da sashe na 29(2)(b) da kuma sashe na 31(2)(e) wanda ya bai wa jam’iyyar damar rushe shugabancinta.

Sannan jam’iyyar ta ce ta kafa kwamitin rikon kwarya a jihar karkashin jagorancin Alhaji Ibrahim Atta, da sakatarenta Barista Baba Lawan, yayin da Ibrahim Aminu Dan Iya, Hajiya Ladadi Dangalan, Aminu Abdullahi Jingau, Muktar Janguza da Abdullahi Isah Sulaiman suke a matsayin mambobi.

PDP ta rushe shugabancin ne bayan ficewar Sanata Kwankwaso daga jam’iyyar a ranar Litinin, inda ta zargi wasu magoya bayansa da neman yi mata sakiyar da ba ruwa.