✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Firai Minista mace ta farko a Samoa ta hau mulki

An shafe wata uku ana rikici da tsohon Firai Minista kan mika wa Fiame mulki.

Fiame Naomi Mata’afa, wadda ita ce tsohuwar Mataimakiyar Firai Minista a kasar ta Samoa, ta fara aiki ne a ranar Talata, inda ta dare kan kujerar tsohon ubangidanta Tuilaepa Sailele Malielegaoi, wanda ya yafe shekara 22 a matsayin Firai Minista, ya kuma yi yunkurin hana ta mulki.

Tuni Fiame mai shekara 64 ta jagoranci zaman farko na Majalisar Ministocin jam’iyyarta ta FAST, ta kuma sanar cewa a shirye suke tsaf su fara aiki.

FILE - In this Sept. 29, 2019, file photo, then Samoa's Prime Minister Tuilaepa Sailele Malielegaoi addresses the 74th session of the United Nations General Assembly at the U.N. headquarters in New York. More than three months after winning an election which sparked a constitutional crisis, Samoa's first female prime minister was finally able to take office on Tuesday, July 27, 2021. After a knife-edge election result in April, Tuilaepa refused to concede defeat, despite several court rulings which went against him. (AP Photo/Kevin Hagen, File)
Tsohon Firai Ministan Samoa, Tuilaepa Sailele Malielegaoi a Babban Taron Majalisar Dinkin Duniya na 74th. (Hoto: AP Photo/Kevin Hagen, tsohuwa ajiya)

Manyan ayyukan da ke gaban sabuwar Firai Ministan sun hada da batun kyautata dangantaka tsakanin kasarta ta China.

Sai dai kuma a lokacin yakin neman zabe ta yi alkawari soke aikin bunkasa tashar jirgin ruwa na Dala miliyan 100 da China take goyon baya a Samoa, bisa hujjar aikin zai kara matsa wa tattalin arzikin kasar da dama can China na bin ta basussuka masu yawan gaske.

An ki ba ta mulki

Bayan lashe zabe a watan Afrilu, Firai Minista Tuilaepa Sailele Malielegaoi ya ki amincewa da shan kaye a hannun Fiame, duk da cewa kotuna daban-daban sun tabbatar da nasarar abokiyar karawar tasa.

A lokacin, manyan na hannun daman Mista Tuilaepa, Shugaban Kasa da kuma Shugaban Majalisar Dokoki sun yi kokarin hana mika wa Fiame mulki.

A watan Mayu an hana Fiame da ’yan jam’iyyarta shiga zauren Majalisar kasar, a yayin da ikirarin cewa shi ne halastaccen Firai Minista. Bangarorin biyu sun zargi juna da yunkurin juyin mulki.

A lokacin ne Firai Minista Fiame da ’ya’yan jam’iyyarta suka karbi rantsuwar kama aiki tare da nada ministoci a wani karamin taro da aka yi a karkashin wata rumfa a gaban ginin majalisar da ke rufe.

A wata hira da aka yi da ita, ta shaida wa kamfanin dillancin labarai na AP cewa, hankalinsu ya tashi a ranar, “Da abubuwa sun lalace, amma muka kai zuciya nesa.”

“Ba don haka ba da mun shiga mun babballa kofofin kamar yadda aka yi a Washington, D.C. Amma muka yi zaman dirshen muna wake-wake da addu’o’i.”

A makon jiya Kotun Kolin Samoa ta yanke hukunci da ke tabbatar da tabbatar da rantsuwar a aka yi wa Firai Minista Fiam wajen Majalisar a matsayi halastacce, daga baya Tuilaepa ya sallama.

Yadda Fiame da Tuilaepa suka raba jiha

A cikin hirar da aka yi da ita, ta ce ta yi murabus ne bayan da ta damu matuka cewa Tuilaepa da takwarorinsa ’yan majalisa sun “sauka daga kan layi” ta hanyar kokarin yin katsalandan a tsarin kotunan kasar da kuma bangaren shari’a.

Fiame ta ce, “Muna ta zamewa daga bin doka, kuma ba na son hakan. Amma yawancin ’yan jam’iyya sun yarda da abin da ake yi.”

Ta ce Tuilaepa bai taba tunanin zai iya faduwa zabe ba, musamman ganin yadda yake da rinjaye a majalisar.

“Ya kadu matuka, har ya kasa gaskata abin da ya faru,” inji ta.

Ana ganin nasarar zaben Fiame a matsayin babban cigaba ba kawai ga Samoa ba, wanda ke da ra’ayin mazan jiya, har ma da yankin Kudancin Pacific, wanda ke da shugabanni mata kadan.

Fiame ta ce ba ta tsammanin jinsinta babban lamari ne a zaben, kuma rawar da ta taka a tsarin mulki na iya zama mafi mahimmanci ga masu jefa kuri’a.

Amma ta yi fatan cewa ta iya zama kyakkyawan abin koyi ga matan Pacific a wasu fannoni sa suke nem cimma burinsu.