✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Fitila ta kona jariri kwana daya da haihuwarsa

Wutar jikin wata fitila da ta fado wa wani jariri mai kwana daya a duniya ta yi sanadin konewarsa a fuska da kafafu a birnin…

Wutar wata fitila da ta fado wa wani jariri mai kwana daya a duniya a birnin Kalaba na jihar Kuros Riba ta yi sanadin konewarsa a fuska da kafafu.

Fitilar ta kuma kona wasu sassan jikin jaririn jim kadan da zuwansa duniya.

Wata ganau a lokacin da abun ya faru mai suna, Misis Stella Aluka ta ce iftila’in dai ya fadawa jaririn ne a falon dakin da aka haife shi saboda mahaifiyarshi ba za ta iya biyan kudin haihuwa a asibitin ba.

A cewarta, fitilar dake haska dakin ce wacce take amfani da kananzir ta yi bindiga tare da kona shi, lamarin da ya yi sanadiyyar samun raunuka da dama a jikinsa.

Tuni dai aka garzaya da jaririn asibitin Victoria a birnin Kalaba inda yake ci gaba da samin kulawa.

Stella ta ce, “Mahaifiyar yaron ta je wani gidan karbar haihuwa ne domin ta haihu a can saboda ba za ta iya biyan kudin asibiti ba. Kwatsam sai fitilar ta fado masa a dakin da aka haife shi.

“Ba zan iya misalta irin wahala da zafin da jaririn yake sha ba ko kuma na mahaifiyarshi a halin yanzu,” inji ta.