✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Fulani da Irigwe sun kulla yarjejeniyar zaman lafiya

Al’ummomin kabilun Fulani da Irigwe da ke Karamar Hukumar Bassa a Jihar Filato, sun sanya hannu kan jarjejeniyar zaman lafiya a tsakaninsu.

Al’ummomin Fulani da Irigwe da ke Karamar Hukumar Bassa a Jihar Filato, sun sanya hannu kan jarjejeniyar zaman lafiya a tsakaninsu.

Shugabannin kabilun biyu sun sanya hannu kan yarjejeniyar ce a gaban Gwamnan Jihar Filato, Simon Lalong, a gidan gwamnatin jihar da ke garin Jos.

Shi dai yankin Bassa, an yi shekaru da dama ana fama da rikice-rikice, tsakanin al’ummomin Fulani da Irigwe.

Da yake jawabi a taron sanya hannu kan yarjejeniyar, Gwamnan Jihar Filato Simon Lalong, ya bayyana farin cikinsa da matakin da al’ummomin suka dauka.

Ya bayyana cewa a taron, shugabannin al’ummomin sun nuna wa duniya cewa sun gaji da rikice-rikice a yankinsu, don haka suka kudiri aniyar yafe wa juna, don kare faruwar rikici-rikice a nan gaba.

Ya yaba wa shugabanni da sauran masu ruwa da tsaki na yankin, kan wannan mataki na zaman lafiya da aka dauka.

A nasa jawabin, Sarkin Miango, Rebaran Ronku Aka, ya gode wa Gwamna Lalong, kan kokarinsa na ganin an sami zaman lafiya a wannan yanki da jihar baki daya.

Ya ce al’ummar Bassa suna son su manta da abubuwan bakin cikin da suka faru a baya, don ganin sun sake dawo da zaman lafiyar da aka san su da shi a da.

A wajen taron, shugabannin kwamitin tsaro da zaman lafiya na Karamar Hukumar Bassa, John Power da Alhaji Ya’u Idris ne suka sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiyar a madadin wadannan al’ummomi.