✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gambiya ta fitar da Guinea daga gasar cin kofin nahiyar Afirka

Gambiya dai ta doke kasar Guinea da ci daya mai ban haushi.

A ci gaba da gasar cin kofin nahiyar Afirka da ke gudana a kasar Kamaru a zagaye na biyu, kasar Gambiya ta fitar da kasar Guinea bayan ta yi nasara a kanta.

A yammacin ranar Litinin ne tawagar kasashen biyu suka kece raini, sai dai Gambiya ce ta yi nasara a kan Guinea da ci daya mai ban haushi.

Dan wasan gaban tawagar ta Gambiya, Musa Barrow, ne ya jefa kwallo a minti na 71, yayin wasan da aka fafata a filin wasa na Kouekong, da ke kasar ta Kamaru.

Har aka tafi hutun rabin lokaci dai, babu daya daga cikin kasashen da ta sami damar jefa kwallo a ragar abokiyar hammayarta.

Yanzu haka dai Gambiya ta samu tikitin zuwa zagaye na uku na gasar ke nan.