✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ganduje ya yi wa fursunoni 90 afuwa

Gwamnan ya yi alkawarin sakin karin fursunoni nan da kwanan 70, wato lokacin Babbar Sallah

Gwamann Jihar Kano, Abdullahi Ganduje ya yi afuwa ga fursunoni 100 a ci gaba da bukukuwan Karamar Sallah a jihar.

Ganduje ya yi musu afuwa ne a yayin ziyarar Sallah da ya jagoranci ’yan Majalisar Zartarwar Jihar Kano tare da shugabannin siyasa da wasu manyan mutane zuwa Gidan Yarin Goron Dutse a ranar Litinin.

Gwamnan ya yi alkawarin “Sakin karin fursunonin nan da kwanan 70, wato lokacin Babbar Sallah,” yana mai umartar wadanda aka sallama da su je gwamnati ta yi musu rajista domin koyon sana’o’in dogaro da kansu.

Sanarwar da kakakin gwamnan, Abba Anwar, ya firtar ta bayyana cewa dalilan yi wa fursunonin afuwa sun hada da: “Rashin lafiya da tsufa da kuma rashin iya biyan tarar da kotu ta yi musu; Har da wadanda aka yanke wa hukuncin kisa.

“Duk da cewa wadansunku an riga an koya musu sana’o’i, masu son samun karin horo su je su yi rajista da gwamnati domin samun wani horo kan sana’o’in dogaro da kai.”

Gwamnan ya bayyana cewa an yi musu afuwa ne domin ba su dama su gyara halayyarsu su zama mutane nagari, gami da rage cunkoso a gidajen yari.