✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ganduje zai ba matashi mafi karancin shekaru mukamin Kwamishina

Matashin zai kasance irinsa na farko da aka taba yi wa mukamin Kwamishina a shekarunsa.

Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya bayar da sunan Dokta Yusuf Jibril JY a matsayin daya daga cikin mutum tara da za a yi wa mukamin Kwamishina a Jihar.

Jibril, ya kasance matashi mafi karancin shekaru daga cikin jerin sunayen wadanda za a nada mukamin sabbin Kwamishinoni a jihar.

Matashin mai shekaru 33 zai kasance irinsa na farko a Jihar Kano da za a yi wa mukamin Kwamishina.

Tuni Majalisar Dokokin Jihar, ta tantance Jibril tare sa wasu mutum takwas, wadanda za a yi wa mukamin Kwamishinoni.

Wannan na zuwa ne bayan ajiye aiki da wasu Kwamishinonin jihar suka yi gabanin shiga zaben fidda-gwani, don neman guraben yin takara a zaben 2023.

Jibril dan asalin garin Rurum ne da ke Karamar Hukumar Rano a Jihar Kano.

Jibril, ya yi karatu har zuwa matakin Digiri, wanda daga nan ne ya shiga harkar kasuwanci, inda ya ke kasuwancin dakon mai a karkashin kamfaninsa mai suna JY Global Services.

Nadin nasa a matsayinsa na matashi zai bude kofa ga matasa musamman wadanda ke rajin ganin an yi tafiya da su a gwamnatance don sharbar romon dimokuradiyya.

Tuni matasa a jihar suka shiga yaba wa Ganduje kan mika sunansa ga majalisar dokokin jihar don tantance shi, inda suke ganin an sanya kwarya a burminta.

Kungiyoyi masu zaman kansu a baya-bayan nan sun sha kiran gwamnatin Jihar da ta yi kokarin jan matasa a jiki don damawa da su.