✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gidauniya za ta sa ’ya’ya mata 150 makaranta kyauta a Yobe

Gidauniyar za kuma ta dauki nauyin karatunsu

Wata gidauniya mai rajin habaka harkar ilimin ’ya’ya mata a jihar Yobe, Hausari female Education support Foundation, za ta saka yara mata 150 makarantun boko kyauta a jihar.

Shugabar gidauniyar, Hajiya Hafsatu Alhaji Ado, ta ce za su ba da tallafin ne a kokarinsu na mara wa aniyar gwamnatin jihar baya wajen inganta ilimim ’ya’ya mata.

Ta bayyana hakan ne a lokacin da take zantawa da wakilinmu a Gombe ranar Lahadi, inda ta ce ciyar da ilimin ’ya’ya mata gaba ne makasudin kafa gidauniyar tasu.

Hajiya Hafsatu ta ce gidauniyar sabuwa ce da aka kirkire ta da manufar yin koyi da kyawawan manufofin gwamnan jihar, Yobe Mai Mala Buni, wajen rage yawan mata da ba sa zuwa makaranta a jihar.

A cewarta, za ta cim ma wannnan buri ne ta hanyar shigar da yara matan makaranta da kuma ta daukar nauyin mayar da wadanda suka daina zuwa makarantar.

Daga nan Hafsatu Ado ta ce bayan mayar da mata 150 sun koma makaranta, za ta sake mayar da wasu 20 din da suka daina zuwa makaranta tare da daukar cikakken nauyinsu.