✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gini mai hawa 10 ya ruguje a Iran

Mutum biyar sun mutu yayin da fiye da 20 sun jikkata.

Wani dogon gini mai hawa 10 a birnin Abadan na Iran ya rushe.

BBC ya ruwaito cewa lamarin ya yi sanadin mutuwar mutum akalla biyar tare da raunata wasu fiye da 20.

Ganau sun shaida wa kungiyar agajin gaggawa ta Iran cewa akwai mutane akalla 80 da suka makale a baraguzan ginin.

Wasu hotuna da aka dauka a Abadan sun nuna mutanen da ke zaune a ginin sun hallara tare da nuna fargaba da fatan zakulo wadanda ba a kai ga ganowa ba.

Kwanaki biyu da suka gabata ne mutum biyu suka mutu yayin da wasu mutum uku suka jikkata a sakamakon rushewar wani gini a yankin Alayaki na Jihar Legas.

Kazalika, kimanin mutum 10 ne suka rasa rayukansu a ranar Lahadi, 1 ga watan Mayu, a sakamakon rushewar wani gini mai hawa uku a Unguwar Ebute Metta da ke birnin Ikkon na Legas.

Hukumomi a Najeriyar na danganta yawaitar rushewar gine-gine da rashin bin tsarin gini da ma rashin ingancin aiki.