✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gobara ta cinye Babbar Kasuwar Mokwa

Wutar da ta fara ci da asubar fari ta kusa cinye ’yan kasuwar da ke kwana a cikin shagunan kasuwar

Dukiya ta makudan kudi ta salwanta a sakamakon wata gagarumar gobara da ta tashi a Babbar Kasuwar Mokwa da ke Jihar Neja.

Gobarar da ta tashi a cikin da asubar fari ta kusa cinye wasu ’yan kasuwar da ke kwana a cikin kantunansu, amma sun sha da kyar da raunuka a jikinsu, an kai su Babban Asibitin Mokwa inda suke samun kulawa.

Basaraken garin, Ndalile-Mokwa, Alhaji Mohammed Shaba, ya ce wutar ta cinye fiye da rabin kasuwar, “Da misalin karfe 4 na asuba, aka kira ni shi ne na kira hukumar kashe gobara. Sun yi ta kokarin kashe wutar, amma saboda rashin motoci, yanzu haka wutar tana nan tana ci.”

Ya ce bata-gari sun yi amfani da damar wajen sace kayan, amma an yi nasarar kama wasu daga cikinsu.