✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gobara ta kashe fursunoni 38 a Burundi

Kawo yanzu ba a bayyana abin da ya haddasa gobarar ba.

Akalla mutum 38 ne suka mutu sakamakon wata gobara da ta tashi a wani gidan yari a Kasar Burundi a ranar Talata.

Mataimakin Shugaban Kasar, Prosper Bazombanza, ya tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai, inda ya ce wasu mutum 69 sun ji rauni.

Rahotanni sun ce gobarar ta tashi ne da misalin karfe 4 na dare, inda wutar ta lalata wurare da dama na ginin gidan yarin.

Sai dai har yanzu ba a bayyana musabbabin tashin gobarar ba, wadda aka samu nasarar kashe ta, zalika babu wani bayani a hukumance kan lamarin.

Gidan yarin na birnin Gitega na dauke da fursunoni sama da 1,500, amma a watan Nuwamba adadin da ya zarce yawan fursunoni 400 da a tsare a gidan.

Yawancin fursunonin da ke gidan yarin maza ne amma kuma akwai bangaren mata.