✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gobara ta kone kwamfuta 100 a Kwalejin Ilimi ta Zariya

Wutar da kone sashen da ake ajiye na'uorin.

Akalla kwamfutoci 100 ne suka salwanta sakamakon wata gobara da ta tashi a Sashen Nazarin Kwamfuta na Kwalejin Ilimi da ke Zariya a Jihar Kaduna.

Jami’an kashe gobara sun yi kokarin kashe wutar da ta tashi da misalin karfe 9 ja safiyar Asabar, lokacin da ma’aikatan kwalejin ba sa aiki.

Shugaban Kwalejin, Dokta Suleiman Balarabe, ya ce wutar ta tashi ne sakamakon matsalar wutar lantarki, wanda hakan ya shafi kayan aikin sashen.

Ya kara da cewa, yana daga cikin tsarin Kwalejin na kashe kayan wutar lantarki a duk lokacin da aka tashi daga aiki, amma ya bada tabbacin za a musanya na’urorin da suka kone.

Har wa yau, ya ce sun dauki matakin kauce wa sake faruwar hakan a gaba.

Ya ce, “Zan sa a fito da wasu kwamfutoci da hukumar TETFund ta ba mu a baya don bai wa dalibai damar ci gaba da amfani na wucin gadi kafin lokacin da za a gyara ginin da ya kone.

“Dole zan gode wa kokarin da ABU Kongo da jami’an kashe gobara na Jihar Kaduna suka yi, wajen kawo mana dauki a kan lokaci.”