✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gombe: Gwamnati za ta samar da litar ruwa miliyan 50 a kullum

Gwamnatin Tarayya da Gwamnatin Gombe ne za su hada gwiwa don samar da kudin aikin

Gwamnatin Jihar Gombe ta ce ta sanya hannu kan wata yarjejeniya tare da Ma’aikatar Albarkatun Ruwa ta Tarayya don samar da ruwan sha.

Yarjejeniyar ta jobanci hada gwiwa a tsakanin gwamnatocin biyu don samar da kudin da ake bukata don inganta da fadada Shirin Samar da Ruwa na Yankin Gombe.

A wata sanarwa da ya fitar, Daraktan Al’amuran Yada Labarai na Jihar ta Gombe, Ismaila Uba Misilli, ya ce manufar yarjejeniyar ita ce gyarawa da fadada Shirin, wanda zai rika samar da lita miliyan 50 ta ruwa a kowace rana

Gwamna Muhammad Inuwa Yahaya ne ya sanya hannu a madadin gwamnatin jihar, yayin da Ministan  Ruwa Injiniya Sulaiman Adamu ya sanya hannu a madadin Gwamnatin Tarayya.