✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gwamnan Kogi: Kotun Koli ta tabbatar da zaben Yahaya Bello

Kotun ta yi watsi da karar da dan takarar jam'iyyar PDP, Musa Idris ya daukaka

Kotun Koli ta tabbatar da nasarar Gwamna Yahaya Bello na Jam’iyyar APC a zaben Gwamnan Jihar Kogi na ranar 16 ga watan Nuwamban 2019.

A safiyar Litinin alkalan Kotun guda bakwai suka sun yi watsi da daukaka karar da dan takarar Jam’iyyar PDP a zaben, Musa Idris ya yi bisa zargin cewa Yahaya Bello bai ci zaben ba.

Alkalin da ta jagoranci zaman, Uwani Abba-Aji, ta ce masu daukaka karar sun kasa tabbatar da zarge-zargen da suka daukaka karar a kai.

Musa Idris na zargin an yi rikicin siyasa a zaben, na’urar tantance masu zabe ba su yi aiki yadda ya kamata ba, sannan kuri’in da aka kada sun fi yawan mutanen da aka tantance a zaben.

Kotun ta ce karar da PD da dan takarata suka daukaka ba ta da amfani saboda sun kasa ayyana rumfunan zabe da jami’an da suka yi aiki a rumfunan da abubuwan da suke zargi sun faru.

Tun da farko Kotun Sauraron Kararrakin Zaben Gwamnan Jihar Kogi wadda ta yi zamanta a Abuja ta yi watsi da zargin dan takarar. Daga baya a watan Agusta Kotun Daukaka Kara ta tabbatar da hukuncin.

Ana dakon hukuncin da alkalan kotun za su yanken game da karar da ‘yar takarar Jam’iyyar SPD a zaben, Natasha Akpoti, ta daukaka, na kalubalantar sakamakon zaben.

Karin bayani na tafe…