✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gwamnati ta yi wa ’yan sanda karin albashi

Gwamnatin ta ce karin zai fara aiki ne daga watan Janairun 2022.

Gwamnatin Tarayya ta amince da yi wa ’yan sanda karin albashi da kaso 20 cikin 100.

Ministan Harkokin ’Yan Sanda, Maigari Dingyadi, ne ya bayyana hakan ranar Laraba, bayan kammala taron Majalisar Zartarwa ta kasa na wannan makon.

Ya ce karin zai fara aiki ne daga watan Janairun 2022.

A cewar Ministan, karin na cikin abubuwan da masu zanga-zangar #EndSARS suka bukata, wanda ke da alaka da walwalar ’yan sanda.

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, wanda shi ne ya jagoranci taron, ya ce za a kara albashin ne don ya dace da ayyukan da suke yi da kuma karfafa yunkurin samar da zaman lafiya a kasa.

Ministan na ’Yan Sanda ya ce za a yi karin ne ta hanyar dada musu kudaden alawus-alawus dinsu da kaso shida cikin 100, da kuma karin Naira biliyan 1.1 don biyan basussukan da suke bi na tsakanin shekarar 2013 zuwa 2020.

Kazalika, Majalisar Zartarwar ta kuma amince da fitar da Naira biliyan 13.1 don biyan kudaden sallamar ’yan sanda 5,472 da suka mutu daga tsakanin shekarar 2013 da watan Agustan bana.