✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gwamnatin Kano ta sanya dokar hana fita

Gwamnatin Kano ta ce sanya dokar hana fitar ta zama dole, saboda dalilan tsaro

Gwamnatin Jihar Kano ta sanya dokar hana zirga zirga a Jihar Kano daga safe zuwa yamma.

Kwamishinan Watsa Labarai, Muhammad Garba ya bayyana a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Kano, cewa sanya dokar ya zama dole saboda guje wa karya doka da oda duba da irin damuwar da aka shiga a lokacin tattara salamakon zaben gwamnan jihar.

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta sanar cewa dan takarar gwamna a Jam’iyyar NNPP, Abba Kabir Yusuf ne ya lashe zabeng gwamnan jihar.

Mataimakin gwamna mai ci, Nasir Yusuf Gawuna, ya zo na biyu, a zaben, wanda kafin sanar da sakamakonsa aka yi ta jira da kananan maganganu.