✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Harin bam ya kashe mutum 12 a masallaci

Kafin harin, gwamnatin Afghanistan da Taliban sun yi yarjejeniyar tsagaita wuta.

Wani harin bam a masallaci ya yi sanadiyyar salwantar rayukan mutum 12 a yayin da suke sallah a kasar Afghanistan.

’Yan sandan Afghanistan sun ce harin ya kawo karshen kwana ukun da kungiyar Taliban ta bayar na tsagaita wuta don murnar Sallah Karama.

Cikin mutane biyun da suka mutu har da limamin masallacin, wasu 15 kuma suka samu rauni.

Da take jawabi jami’ar yada labaran rundunar ’yan sandan yankin Shakar Darah, Ferdaws Framurz, ta ce ’yan ta’addan sun kai harin bam ne cikin masllacin ne a daidai lokacin da ake tsaka da yin Sallah.

Wannan hari dai shi ne na farko tun bayan da mayakan Taliban sun ba da sanarwar tsagaita wuta na kwana uku saboda bai wa jama’a damar gudanar da bikin Sallah Karama cikin kwanciyar hankali.

Afghanistan, na daga cikin kasashen da ke fuskantar yake-yake, tun bayan ficewar dakarun sojin kasar Amurka daga kasar.

Gwamnatin kasar ta shafe sama da shekara 10 tana yaki tsakaninta da Taliban, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da dama.