✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Harin bom ya kashe mutum 18 a masallaci a Afghanistan

Ana fargabar yiwuwar samun karuwar wadanda za su iya mutuwa sakamakon tashin bom din.

Akalla mutum 18 ne suka riga mu gidan gaskiya sakamakon wani mummunan harin bom da ya auku a wani masallacin Juma’a a Yammacin kasar Afghanistan.

Wani bidiyo da a yanzu ya karade kafofin sadarwa ya nuna gawarwakin mutane barbaje a harabar masallacin yayin da jini ya zama tamkar abun shimfida a daben masallacin.

Kakakin gwamnatin birnin na Herat, Hameedullah Motawakkel ya ce baya ga mutum 18 da suka mutu a harin akwai kuma wasu 21 da suka samu muggan raunuka wadanda tuni aka mika su ga asibiti mafi kusa.

Daga cikin wadanda suka mutu sakamakon harin a masallacin Guzargah da ke a birnin Herat har da wani fitaccen malami addinin Islama daya daga cikin ’yan gaba-gaba masu goyon bayan gwamnatin Taliban, Mujib-ul Rahman Ansari.

Mujib-ul Rahman Ansari shi ne wanda a farkon wannan shekara ya yi kiran da a fille kan duk wani da ya karya dokar gwamnatin Afghanistan ta yanzu komai kankanta.

Kakakin gwamnatin Taliban, Zabihullah Mujahid da ke tabbatar da kisan Mujib-ul Rahman a harin na Juma’ar nan, ya bayyana fitaccen malamin a matsayin wanda ya yi shahada.

Bayanai sun ce ana fargabar yiwuwar samun karuwar wadanda za su iya mutuwa sakamakon tashin bom din.

A baya bayan nan dai an samu saukin tashin husuma a Afghanistan tun bayan karbe gwamnati da Taliban ta yi a bara, sai dai ana ci gaba da samun tashin boma-bomai nan da can; lokaci zuwa lokaci.

A watan da ya gabata, wani harin bom da kungiyar IS ta dauki alhakin kai wa wani masallaci a birnin Kabul, ya kashe wani malami da ke goyon bayan gwamnatin ta Taliban.