✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Harin Jirgin Kasa: Mutum 68 na tsare a hannun ’yan bindiga 

'Yan bindigar na rike da mata 41 da maza 22, sai kuma yara biyar.

Akalla mutum 68 rahotanni ke cewa na hannun ‘yan bindigar da suka kai hari jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna a ranar 28 ga watan Maris.

Wani bidiyo da aka fitar wanda ya rinka yawo har a kafofin sada zumunta, na tabbatar da cewa ‘yan bindigar na rike da mata 41 da maza 22, sai kuma yara biyar.

Wannan na zuwa ne mako biyu bayan kai kazamin harin bam a jirgin da ya tashi daga Abuja zuwa Kaduna, mutane da dama sun rasa rayukansu baya ga wadanda aka jikkata.

Mako guda bayan harin hukumar da ke kula da zirga-zirgar jiragen kasa a Najeriya ta fitar da sanarwar da ke cewa har yanzu akwai fasinjoji 146 da ba a ji duriyarsu ba.

Sai dai shugaban Bankin Manoma, Mallam Alwan Hassan, da ya samu kubuta a makon da ya gabata shi ya ba da alkaluman mutanen da ke hannun ‘yan bindigar a lokacin da ya ke bayani kan halin da ya tsinci kansa.

Bayan kai harin, Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya ce sun san da cewa za a kai harin, sannan ya shaida cewa dama mayakan Boko Haram yanzu na cin karensu babu babbaka a dazukan yankunan Kaduna har zuwa Neja.