✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Harin kunar bakin wake ya kashe mutum 34 a masallaci a Pakistan

Akwai fargabar a samu karuwar asarar rayuka.

Mutum akalla 34 yanzu haka aka tabbatar sun mutu a sakamakon wani kazamin harin kunar bakin wake da wani ya kai kan masu ibada a masallaci a Pakistan.

Rundunar ’yan sandan kasar Pakistan ta sanar da hakan tana mai bayyana kazamin hari a matsayin ta’addanci.

Sanarwar rundunar ta kara da cewa, maharin ya tayar da abin fashewa ne a cikin wani masallaci da ke daf da harabar ginin ofishin ’yan sanda a kusa da birnin nan na Peshawar.

Kafofin watsa labarai da dama sun ruwaito cewa akasarin ginin masallacin ya rushe tare da danne masu ibada.

Akwai fargabar a samu karuwar asarar rayuka ta la’akari da munin harin da ya raunata wasu fiye da dari.

Akasarin wadanda suka mutun jami’an ’yan sanda ne, kawo yanzu babu kungiyar da ta fito ta dauki alhakin kai harin a kasar da ta jima tana fama da hare-hare masu nasaba da ta’addanci.